ALAƘAR SHA'AWA DA ZUCIYAR MACE
Shi Namiji Soyayya da Sha'awa Abune Mabanbanta wajensa, Dan haka Zai Iya Sha'awa Kaɗai ko ba Soyayya, ita kuma Mace Soyayya da Sha'awa Haɗe Suke Zuciyarta, Inhar ta Ƙaunaceka zatai Sha'awarka, Sannan Bazatai Sha'awarka ba Sai in Tana Sonka.(A Asalin Daɓi'arta)
Kasantuwar Alaƙa mai karfi dake tsakanin So da Sha'awarsu yasa suke da Wuyar sha'ani, Domin sha'awa abune dake da Hatsari sbd Yadda take control ɗin mutum, Mace Inhar ta kamu So yana wuya wani abu ya hanata isa ga abun Sonta, kuma duk Yadda zatai na mallakarsa ko sashi farin ciki zatai ba ruwanta koda ckn haka akwai Saɓon Allah😥, Ya isa Misali kaga mai ilimi ta afka zina, ko kaji Ustaziya tayi hirar tayi hirar Romance😢 dss. Sbd So da Sha'awa abune cakude a sha'aninsu (koda matar aure ce).
Sai Yasa yana da muhimmanci Musan... Su Mata ba banbanci tsakanin budurwa da matar aure wajen afkawa Son Wani Namiji Inhar Sukaga Dalilin Son a tare dashi, haƙuri ne kawai da Juriya da Imani Ke Tasiri a wannan waje(من مَن عصمهن الله), Amma inba haka ba aure baya hana mace Jin son wani Namijin Inhar taga dalilin so a tare dashi,(Allah ya tsare matanmu).
Abunda zai tabbatar mana haka...
Zulaikha Matar Azizu Misr tana matar Aure Ta Kamu da son Annabin Yusuf(A.S)
قد شغفها حبا
So da Sha'awarsu mata Haɗe suke, sai yasa daga kamuwa da Sonsa Sai ta sallama masa kanta
وَغَلَّقَتِ الْأَبْوَابَ وَقَالَتْ هَيْتَ لَكَ
Daga wani abu daya kamata mu sani...
Tasirin sha'awar mace a Soyayyarmu da zamantakewarmu Shike sasu Jara'ah(karfin halinsun nan) ckn aikata ba daidai ba(da gangan) ko cutarwa ko rashin mutunci, ga Abokan zamansu tare da azuciyarsu akwai Son😃 haka na faruwa Inhar ka Gaza a mata wata buƙata ckn bukatunta na Rayuwa,
Misali Zulaikha "Ɗa" Take So, tare da tana son Annabi Yusuf hakan bai hanata Cakumo shi Suyi lalata ba(da yaqi ckn sauki) bayan ya ƙwace ya gudu kuma ta biyo shi harta yaga masa riga Dukda Nufin (Kota Ƙarfi) ya biya mata buƙata😥
وَاسْتَبَقَا الْبَابَ وَقَدَّتْ قَمِيصَهُ مِنْ دُبُرٍ
Naka da sauki in ya tsaya a ƙin yin girki, ko Shariya ko rashin kunya dss.
Mata So da Sha'awa na sasu Ƙarya dayin abu gaba Gaɗi ba tare da lura da mai zai biyo baya ba, koda suna sonka, Kmr yadda Zulaikha ma tayi
مَا جَزَاءُ مَنْ أَرَادَ بِأَهْلِكَ سُوءًا إِلَّا أَنْ يُسْجَنَ أَوْ عَذَابٌ أَلِيمٌ
Da faɗinta
وَلَئِنْ لَمْ يَفْعَلْ مَا آمُرُهُ لَيُسْجَنَنَّ وَلَيَكُونًا مِنَ الصَّاغِرِينَ
Toh amma Hakan bamai tabbata bane, na wani lokaci ne, sai yasa itama Zulaikha Lokacin da Sha'awar ta ragu bayan ma tsawon shekaru bata ganin Annabi Yusuf (yana kurkuku), da kanta ta bayyana kuskurenta Gaban kowa
قَالَتِ امْرَأَتُ الْعَزِيزِ الْآنَ حَصْحَصَ الْحَقُّ أَنَا رَاوَدْتُهُ عَن نَفْسِهِ وَإِنَّهُ لَمِنَ الصَّادِقِينَ
Sbd Ita Mace Duk yadda takai ga maka ba daidai ba Inde da son, bata lokaci daga baya zaka ga tayi nadama, Faɗinta
ذَٰلِكَ لِيَعْلَمَ أَنِّي لَمْ أَخُنْهُ بِالْغَيْبِ وَأَنَّ اللَّهَ لَا يَهْدِي كَيْدَ الْخَائِنِينَ
Malamai suka ce wannan son nasa ne de tare da tsawon shekarun😢(tunda ance harta fara tsufa) amma soyayyar ta sa ta haka.
Mata kenan da soyayya!!
Dan haka mu karanci zuciyar mata, Hakika su Littafai ne da ba'a musu Hukunci da ganin bangon, dole sai an karanta su.
Wannan shine Ɗan Abunda zamu Faɗa A wannan Babi, Allah ya mana muwafaqa. AMIN